fidelitybank

Fiye da Mutane 26 na hannun ‘Yan Bindiga a Zamfara

Date:

‘Yan bindigar da suka mamaye garin Sabon Gari a ƙaramar hukumar Ƙaurar Namoda sun kashe aƙalla mutum uku tare da yin garkuwa da 26 da suka haɗa da mata da yara ƙanana.

Maharan da jaridar Daily Trusta ruwaito cewa magoya bayan ɗan bindigar nan ne Bello Ƙaura da aka fi sani da Ɗan Sade, da ake ta’allaƙawa da munanan hare-haren da suka addabi ƙananan hukumomin Ƙaurar Namoda da Maradun.

Rahotannin sun tabbatar da cewa mazauna garuruwan Kungurki da Sabon Gari da Uguwar Sarkin Musulmi da Unguwar Rogo da Yamatsiwa sun tsere daga gidajensu domin gujewa hare-haren ‘yan fashin dajin.

A ranar Jumu’a ma wasu ‘yan bindiga sun kashe aƙalla mutum huɗu a yankin ciki har da sakataren ƙaramar hukumar Birnin Magaji inda nan ma wasu maharan suka yi garkuwa da ƙarin wasu mutum biyu.

Majalisar dokokin jihar Zamfara dai a baya ta bayana fatan hukumomin sojojin ƙasar su kai wa ƴanfashin hari cikin sansanoninsu da ke dajin Gando da ƴarjiji da Mazaro, kamar yadda a baya a ka kai hari kan sansanonin ƴan bindigar a dazukan Zurmi da Tsafe tare kuma da sanya shingayen binciken jami’an tsaro tun daga Mayinci har zuwa garin Gummi.

Jihar Zamfara dai na sahun gaba cikin jerin jahohin arewa maso yamma da ke fama da harin ‘yan bindiga waɗanda kisan jama’a da ƙona amfanin gona tare da garkuwa da mutane.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp