‘Yan bindigar da suka mamaye garin Sabon Gari a ƙaramar hukumar Ƙaurar Namoda sun kashe aƙalla mutum uku tare da yin garkuwa da 26 da suka haɗa da mata da yara ƙanana.
Maharan da jaridar Daily Trusta ruwaito cewa magoya bayan ɗan bindigar nan ne Bello Ƙaura da aka fi sani da Ɗan Sade, da ake ta’allaƙawa da munanan hare-haren da suka addabi ƙananan hukumomin Ƙaurar Namoda da Maradun.
Rahotannin sun tabbatar da cewa mazauna garuruwan Kungurki da Sabon Gari da Uguwar Sarkin Musulmi da Unguwar Rogo da Yamatsiwa sun tsere daga gidajensu domin gujewa hare-haren ‘yan fashin dajin.
A ranar Jumu’a ma wasu ‘yan bindiga sun kashe aƙalla mutum huɗu a yankin ciki har da sakataren ƙaramar hukumar Birnin Magaji inda nan ma wasu maharan suka yi garkuwa da ƙarin wasu mutum biyu.
Majalisar dokokin jihar Zamfara dai a baya ta bayana fatan hukumomin sojojin ƙasar su kai wa ƴanfashin hari cikin sansanoninsu da ke dajin Gando da ƴarjiji da Mazaro, kamar yadda a baya a ka kai hari kan sansanonin ƴan bindigar a dazukan Zurmi da Tsafe tare kuma da sanya shingayen binciken jami’an tsaro tun daga Mayinci har zuwa garin Gummi.
Jihar Zamfara dai na sahun gaba cikin jerin jahohin arewa maso yamma da ke fama da harin ‘yan bindiga waɗanda kisan jama’a da ƙona amfanin gona tare da garkuwa da mutane.