Annobar korona ta sa an fasa auren Firaiministar ƙasar New Zealand, wanda sai nan gaba za a sanar da sabon lokacin da za a yi auren.
New Zealand ta sanya dokar takaita taruwar jama’a na kar su haura mutum 9, bayan samun wadanda suka kamu da cutar korona nau’in Omicron a wani gidan biki.
Fira Minista Jacinda Ardern, ta ce, daga tsakar daren ranar Lahadi, dokar taruwar mutane 100 a wajen biki ta na aiki, amma wadanda suka yi rigakafin korona za ta fara aikin, ya yin da wadanda ba su yi rigakafin ba, ba za su haura mutum 25 ba.
Mis Ardern tabbatar da cewa, “Saboda halin da ake ciki ni kai na, an dage lokacin aure na”
Mutum 9, iyalan gida guda aka gano sun kamu da nau’in Omicron, wadanda suka taso daga Auckland, domin halartar biki a New Zealand.