fidelitybank

Fintiri ya yi tir da jami’in INEC

Date:

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya ce, ya ji takaicin abin da shugaban hukumar zaɓe na Jihar Farfesa Hudu Yunus Ari, ya yi na ayyana abokiyar takararsa a matsayin wadda ta lashe zaɓen jihar tun gabanin a kammala tattara sakamako.

Ya ce tuntuni sun yi hasashen hakan zai iya faruwa, shi yasa suka yi ƙorafin a cire shi daga harkokin gudanar da zaɓen domin ba zai yi musu adalci ba, domin sun ga abin da ya faru a Sokoto.

“Shi yasa muka yi ta kira ga INEC ta cire shi, saboda mun ga abin da wancan ya yi a Sokoto, muka yi fargabar kada ya yi mana a nan.

“Sun yi abin da ya kamata domin jiya sun cire shi sun kawo kwamishina wanda shi ya aiwatar da ayyuka yadda ya kamata,” in ji gwamna Fintiri.

Ya ce abin mamakin shi ne Farfesa Hudu ya je cikin mutane yana cewa “bai ji daɗi ba da aka cire shi jiya ba, amma yau zai aikta abin da yake so,”.

A cewarsa “Babu sakamako a hannunsa babu takarda cewarsa kawai ya ba wa wance ta ci zaɓe,” abin da ya bayyana a matsayin abin takaici.

Fintiri ya yaba wa INEC kan matakin da ta ɗauka cikin gaggawa, na dakatar da karɓar sakamakon zaɓen gwamnan jihar ta Adamawa.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp