Shugaban Turkiyya Racip Tayyib Erdogan, ya tattauna da shugabannin Sweden da Finland ta wayar tarho.
Yayin tattaunawar ta su, Erdogan ya bukaci su dauki matakin da ya dace na kawo karshen goyon bayan da suke bai wa abin da ya kira kungiyoyin ” ‘yan ta’adda”.
A wannan makon ne kasashen biyu suka nemi su shiga kungiyar ƙawancen tsaro ta Nato.
Sai dai Turkiyya wadda ita ma mamba ce a kungiyar, ta yi barazanar kawo tsaiko ga bukatar tasu, wadda ke neman amincewar duka mambobin kungiyar.
Erdogan ya zargi kasashen biyu da goyon bayan mayakan Ƙurdawa, da kuma kungiyar ‘yan aware ta PKK.