Wani matashi Mai Suna John ya koma addinin musulci, sakamakon Kallon shirin nan mai dogon zango mai suna Izzar So.
Mashiryin kuma jarumi a cikin shirin Izzar So, Lawan Ahmad ne ya bayyana hakan a sashin shafinsa na Facebook.
“Masha Allah a yaune mu ka yi babban kamu a musulunci, inda wannan bawan Allah ya shiga musulunci, saboda kallon IZZAR SO da ya ke yi, tun daga Cross River, Idom Ikon karamar hukumar ta Cross River, a yanzu haka dai ya Karbi musulunci, kuma yanzu haka sunansa ya koma, Umar Daga John, mun yi masa addu’a Allah yasa ya shigo addinin musulunci a sa a Allah yasa ya amfane shi, amin” in ji Ahmad Lawan.
Al’umma da dama dai suna kallon shirin ne na Izzar So, Saboda yadda ya ke fadakarwa ta fuskar addinin musulci da riko da gaskiya da amana.