Hukumar da ke kula da kwallon kafa ta duniya, FIFA, a ranar Litinin, ta kakabawa Najeriya takunkumi kan rashin da’a da magoya bayanta suka yi a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da Ghana a Abuja wanda a ka yi a ranar 29 ga Mayu, 2022.
Kwamitin ladabtarwa na FIFA ya ci tarar Najeriya Sefa CHF 150,000 kwatankwacin Naira miliyan 63.9, biyo bayan tashin hankalin da ya faru a filin wasa na Moshood Abiola na kasa, Abuja bayan da kasar ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya a Qatar a 2022.
Haka kuma sun umarci kasar da ta buga wasansu na gaba na kasa da kasa a bayan fage, wanda hakan ke nufin kungiyar ta Najeriya za ta buga ba tare da ‘yan kallo ba.