FIFA ta yi barazanar haramtawa Tunisia shiga gasar cin kofin duniya ta 2022, bayan kalaman ministan wasanni na kasar.
Tunisia na fuskantar barazana bayan da ministan matasa da wasanni, Kamel Deguiche, ya yi magana game da yiwuwar “rusa ofisoshin tarayya na fannoni daban-daban”.
Da alama FIFA ta dauki hakan da nufin hukumar kwallon kafa ta Tunisia (FTF).
A wata wasika da aka fitar, wacce gidan rediyon Mosaique FM ta buga, hukumar kwallon kafa ta duniya ta bukaci a yi karin haske kan wadannan kalamai.
Wasikar ta yi nuni da “yunkurin hukumomin kasar na tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Tarayyar Tunisiya da kuma barazanar da take yi na rusa ofishin FTF”.
FIFA ta yi gargadin cewa mambobinta “ya wajaba a kan doka su gudanar da harkokinsu ba tare da wani tasiri ba daga wasu bangarori na uku.”
Ya kara da cewa rashin bin umarnin “na iya haifar da zartar da hukunci a karkashin dokokin FIFA, gami da dakatar da kungiyar da ta dace.”