Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ranar Talata, ya karɓi baƙwancin gwamnonin jam’iyyar APC guda biyu a fadarsa dake babban birnin tarayya Abuja.
Daily Trust ta rawaito cewa, gwamnonin sune, Atiku Bagudu na jihar Kebbi, shugaban kungiyar gwamnonin APC a karo na biyu da kuma Muhammad Badaru na jihar Jigawa.
Gwamnonin sun gana da shugaban ƙasa Buhari ne dangane da babban gangamin APC na ƙasa dake tafe ranar 26 ga watan Fabrairu, wanda za’a zaɓi shugabannin jam’iyya a matakin ƙasa.
A ranar Alhamis da ta gabata, jam’iyyar APC ta rantsar da sabbin shugabanninta na jihohi yayin da take fuskantar babban taro.
Ƙungiyoyi da dama na cigaba da taro kala daban-daban a wani yunƙurin da suke na ganin wanda suke goyon baya ya samu nasara. Sai dai a ɓangaren shugaban ƙasa Buhari ya yi gum da bakinsa game da wanda yake so ya zama shugaban jam’iyya na ƙasa da kuma wanda zai gaje shi a 2023 dake tafe.