fidelitybank

Fetur mallakin al’ummar Neja-Delta ne ban a Najeriya ba – Cif Ayo  

Date:

Mukaddashin shugaban kungiyar ra’ayin jama’a ta kabilar Yarabawa, Afenifere, Cif Ayo Adebanjo, ya caccaki kalaman da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya yi na cewa man da ke yankin Neja-Delta na Najeriya ne, inda ya ce albarkatun na al’ummar yankin ne.

Dattijon ya kuma yi mamakin ko tsohon shugaban kasar ya na cewa, Allah ne ya halicci albarkatun Neja-Delta lokacin da Najeriya ta kafu a shekarar 1914, ko kuma a can ne kafin hadewar?

Obasanjo ya bayyana hakan ne a cikin wani rahoto da jaridu ta fitar inda ya ce, man da ke yankin Neja Delta na Najeriya ne, kuma yunkurin da Cif Edwin Clark ya yi na ganin an daidaita lamarin ya ci tura bayan sanarwar da Areas Consultative Forum (ACF) ke goyon bayan matsayin tsohon shugaban kasar.

Cif Adebanjo ya tabbatar da hakan ne a ranar Larabar a wani taron manema labarai da ya gudana a gidansa da ke Legas, wanda ya samu halartar sauran shugabannin kungiyar Afenifere da suka hada da Sanata Femi Okurounmu, Cif Supo Shonibare, Farfesa Ebun Sonaya, Cif Tunde Onakoya, Cif Lanre Anjolaiya, Alhaji Abdullahi Adebayo. Inaolaji, Ms Nike Olujemibola da Jare Ajayi, mai magana da yawun kungiyar ta Afenifere.

Shugaban na Afenifere ya bada misali da kundin tsarin mulki na 1960 da 1963 wanda ya tabo batun rabon kudaden shiga wanda a halin yanzu ake kiransa da kula da albarkatun kasa, yana mai cewa kundin tsarin mulkin 1963 ya bada damar biyan kashi 50 cikin 100 a sashe na 140, zuwa yankin da aka samu kudaden shiga.

 

 

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp