fidelitybank

Fetur mallakin al’ummar Neja-Delta ne ban a Najeriya ba – Cif Ayo  

Date:

Mukaddashin shugaban kungiyar ra’ayin jama’a ta kabilar Yarabawa, Afenifere, Cif Ayo Adebanjo, ya caccaki kalaman da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya yi na cewa man da ke yankin Neja-Delta na Najeriya ne, inda ya ce albarkatun na al’ummar yankin ne.

Dattijon ya kuma yi mamakin ko tsohon shugaban kasar ya na cewa, Allah ne ya halicci albarkatun Neja-Delta lokacin da Najeriya ta kafu a shekarar 1914, ko kuma a can ne kafin hadewar?

Obasanjo ya bayyana hakan ne a cikin wani rahoto da jaridu ta fitar inda ya ce, man da ke yankin Neja Delta na Najeriya ne, kuma yunkurin da Cif Edwin Clark ya yi na ganin an daidaita lamarin ya ci tura bayan sanarwar da Areas Consultative Forum (ACF) ke goyon bayan matsayin tsohon shugaban kasar.

Cif Adebanjo ya tabbatar da hakan ne a ranar Larabar a wani taron manema labarai da ya gudana a gidansa da ke Legas, wanda ya samu halartar sauran shugabannin kungiyar Afenifere da suka hada da Sanata Femi Okurounmu, Cif Supo Shonibare, Farfesa Ebun Sonaya, Cif Tunde Onakoya, Cif Lanre Anjolaiya, Alhaji Abdullahi Adebayo. Inaolaji, Ms Nike Olujemibola da Jare Ajayi, mai magana da yawun kungiyar ta Afenifere.

Shugaban na Afenifere ya bada misali da kundin tsarin mulki na 1960 da 1963 wanda ya tabo batun rabon kudaden shiga wanda a halin yanzu ake kiransa da kula da albarkatun kasa, yana mai cewa kundin tsarin mulkin 1963 ya bada damar biyan kashi 50 cikin 100 a sashe na 140, zuwa yankin da aka samu kudaden shiga.

 

 

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp