Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United a mako mai zuwa, inda yake tunanin komawa Al-Hilal ta Saudiyya waɗanda suka yi masa tayin albashi mai tsoka.
An bayyana cewa wakilan Fernandes sun gana da jami’an Al-Hilal cikin kwanaki da suka gabata domin samun mafita da za ta kai ga ɗan wasan mai shekara 30 ya koma ƙungiyar.
Batun dai na janyo muhawara a kafofin sada zumunta a daidai lokacin da Man Utd ɗin tayi balaguro zuwa nahiyar Asiya don buga wasannin sada zumunta. Latsa nan domin karanta cikakken labarin