Ayodele Fayose, tsohon gwamnan jihar Ekiti ya caccaki wasu masu neman takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jamâiyyar PDP, ya kuma sha alwashin ba zai taba barin kujerar ba ga kowa.
Fayose ya caccaki irin su tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dr. Bukola Saraki, kan neman tikitin PDP tilo a zaben 2023.
A cewar tsohon gwamnan, da ace Atiku da Saraki sun tsaya a PDP a shekarar 2015 suna goyon bayan tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan duk da kura-kurai da yake da shi, da APC ba za ta ci zaben shugaban kasa ba.
Ya yi nuni da cewa Saraki da Atiku sun koma PDP ne kawai, saboda ba su yi nasara a APC ba, yana tunanin ko sun dawo PDP da sun zama shugaban kasa alhalin suna APC.
Da yake bayyana hakan a Talabijin na Channels, ranar Laraba, Tsohon Gwamnan ya ce, âBari in dauki misali da shugabanmu mai daraja, Alhaji Atiku Abubakar, wanda ya yi nasara a Adamawa da kuriâu kasa da 20,000 a 2019, shi kuwa Bukola ba mu ci komai a Kwara ba.