Fasto Yahaya Dikko na Cocin Evangelical Winning All (ECWA) Kaduna, wanda aka yi garkuwa da shi ya tsere daga gidan masu garkuwa da mutane.
Kubucewar tasa na zuwa ne watanni biyu bayan da aka yi garkuwa da shi a Sabon Kurutu da ke karamar hukumar Kachia a jihar Kaduna.
Wani shugaban al’umma a yankin, Mista Makeri Danjuma Mohammad, wanda ya tabbatar da tserewarsa, ya ce masu garkuwa da Fasto sun ki sakinsa bayan sun karbi kudin fansa da babura na Naira 800,000.
“Wannan Fasto Yahaya D Dikko ne na Cocin ECWA Sabon Kurutu da ke Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna. An sace shi kimanin watanni biyu da suka gabata. An biya kudin fansa amma masu garkuwa da mutane sun dage cewa sai an kawo babur da ya kai Naira 800,000 kafin a sake shi,” inji shi.
A cewarsa, Fasto ya tsere ta hanyar mu’ujiza, inda ya kara da cewa an kai shi wani asibiti da ba a bayyana ba domin yi masa magani.