‘Yan ta’addan da suka kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar Litinin, sun shaida wa iyalan wadanda aka sace da su shirya su biya musu kuɗin abinci da kuma biyan bukatunsu na kudin fansa.
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Najeriya NRC, ta ce, fasinjoji 362 ne ke cikin jirgin a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari, inda suka kashe 8, suka jikkata 26 tare da yin awon gaba da wasu da dama.
Musa Abilewa, daya daga cikin iyalan wadanda abin ya shafa, ya bayyanawa DAILY POST ranar Alhamis, cewa ya samu kiran waya da yammacin Laraba daga ‘yan ta’addan.
Ya tabbatar da cewa dan uwansa da aka sace ba shi da lafiya, amma an ce masa ya shirya domin neman biyan kudin fansa.