Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya nemi gafara al’umma bisa hare-haren da ‘yan bindiga da ke ci gaba da salwantar da rayukan a yankunan Jihar Kaduna, musamman harin da aka kai wa jirgin kasa a ranar Alhamis.
Gwamnan, wanda cikin yanayi mai cike da damuwa ya ce, haƙiƙanin gaskiya yana cikin matuƙar bakin ciki, saboda rabonsa da ya yi bacci tun ranar Alhamis, kuma ba ya iya bacci ko da ya sha maganin bacci, saboda tsananin tashin hankali.
El-Rufa’i ya yi waɗannan kalamai ne lokacin da ya je karamar hukumar Giwa domin bai wa al’umma hakuri da ta’azziya da jaje bisa abubuwan da ke faruwa.
Ya kai ziyarar ne ranar Alhamis ƙarƙashin rakiyar mataimakiyarsa Hajiya Hadiza Sabuwa Balarabe da kuma wasu mukaraɓan gwamnatinsa.
A wani saƙon murya da masu taimaka wa gwamnan kan yaɗa labarai suka bai wa BBC, gwamnan ya ce, hakkin shugabanci abu ne da wata rana zai tashi ya tsaya gaban Ubangiji, domin ya yi bayyani kan abubuwan da ke faruwa da abubuwan da ya aiwatar.