fidelitybank

Fasa rumbunan abinci babban laifi ne – Minista

Date:

Ƙaramar ministar Abuja ta bayyana ayyukan fasa rumbun ajiye abinci da wasu mutane suka yi a birnin da cewa babban laifi ne.

Dr. Mariya Mahmoud ta bayyana hakan ne bayan kai ziyarar gani da ido don shaida irin ɓarnar da aka yi a wajen ajiye abincin da aka tatuke.

A shafinta na X ta wallafa cewa: “Na je rumbun ajiye abinci a Gwagwa-Tasha don tantance irin ɓarnar da zauna-gari-banza suka yi a ranar Lahadi. Wannan abin ya wuce yunwa, babban laifi ne!!!

Abin da na gani abu ne mara daɗi, yanayi ne da wasu zauna -gari-banza suka wawushe duka hatsain da sauran kayan abinci da ke wurin…

Wani ɗankasuwan da BBC ta zanta da shi a unguwar karmo da ke birnin, ya bayyana cewa mutane sun wawashe masa kayan abinci a wurin ajiyar kayan da ke Karmo.

Mutumin ya ce lamarin da ya faru a ranar Lahadi, ya janyo masa asarar sama da naira miliyan 100.

Yayin da mutanen da ke maƙwaftaka da wurin suka bayyana yadda masu fasa rumbun suka zo da da makamai da suka haɗa da adduna da sanduna da wuƙaƙe wajen fasa rumbun.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp