Babbar Kotun Tarayya da ke zaman ta a jihar Legas, ta yanke wa wani tsohon jami’in Hukumar Kwastam tare da wasu mutum biyu hukuncin daurin shekara 16, bisa laifin shigo da bindigogi 661 ba bisa ka’ida ba.
Mai Shari’a Ayokunle Fajji, ta sami Mahmud Hassan da kamfaninsa da Oscar Okafor da kuma Donatus Achinulo da laifin hada baki wajen yin fasakwaurin bindigogin.
Aminya ta rawaito cewa, sai dai kotun ta wanke tare kuma sallamar daya daga cikin wadanda a ke tuhuma, Abdullahi Danjuma daga dukkan zarge-zargen da a ke yi masa.
A cikin kunshin tuhume-tuhumen da a ke musu, Babban Lauyan Gwamnati, kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya zarge su da shigo da makaman daga kasar Turkiyya ta tashar jiragen ruwa ta Apapa da ke Legas.
Ya ce,”An shigo da bindigogin ne a cikin wata kwantena mai zurfin kafa 40, wadda a ka yi karyar cewa kamaren karfe ne a cikinta”. Inji Malami.