fidelitybank

Fasa Kauri: Kwastam ta kama kayan sama da Naira miliyan 854 a Kano

Date:

Hukumar hana fasa kauri ta kasa Kwastam, ta kama haramtattun kayayyaki da su ka kai sama da Naira miliyan 854 a cikin watanni Uku.

Mataimakin Kwanturola, Oseni Olorukooba, kodinetan hukumar kwastam mai kula da jihohin Kano da Jigawa, ya bayyana cewa masu fasa kaurin a yanzu ba su da wata mafaka da za su kai ga aikata muggan laifuka.

Ya ce,”Kayayyakin da a ka kama sun hada da motoci biyu, buhunan shinkafar kasar waje 413 da kuma bale 382 na kayan sawa. Sauran sun hada da katan 150 na macaroni, katon spaghetti 200, katuna 638 na takalman kasashen waje masu girma dabam na yara, maza da mata”.

Ya bukaci kafafen yada labarai da su ci gaba da fadakar da jama’a kan illolin da ke tattare da safarar kayayyakin da aka haramta a cikin kasar nan.

Ko’odinetan ya kuma jaddada aniyar rundunar na yaki da fasa kwauri.

Olorukuba ya kuma yabawa jami’an hukumar da kuma jami’an hukumar bisa samun nasarorin da a ka samu a tsawon lokacin da a ke bitar.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp