fidelitybank

Farashin man fetur ya tashi – IPMAN

Date:

Dillalan man fetur ta ƙasa IPMAN, sun ce, farashin man fetur ya ƙaru zuwa naira 720 a kan lita ɗaya daga naira 651, a wani lamari da ya sanya tashoshin sauke mai suka kasance tamkar babu kowa

Wannan a cewar dillalan man ya samo asali ne daga yawan sauyin da ake samu na darajar kuɗaɗen waje.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa dillalan man fetur su ma sun bayyana cewa gidajen mai da dama na rufewa a kullum yayin da kasuwar sayar da mai ke ƙara tabarbarewa.

Sun ce hakan na iya haifar da matsalar karancin man fetur a cikin watanni masu zuwa.

Da yake jawabi a wurin taron shugabannin kungiyar masu samar da man fetur da iskar gas ta Najeriya, a Abuja ranar Alhamis, shugaban ƙungiyar, Benneth Korie, ya ce a halin yanzu harkoki sun tsaya a tashoshin sauke man fetur masu yawa.

Shi ma shugaban kamfanin PETROCAM Trading, Patrick Ilo da yake zantawa da jaridar, ya bayyana cewa kudin man fetur da suka shigo da shi metrik tan 52,000 a ranar Talata, ya kai naira 720 duk lita daya ba tare da tallafin hukuma.

A cewarsa, matukar farashin man fetur ya kai naira 720 duk lita daya a tashoshin sauke man fetur, to mai yiwuwa ne kudin lita daya zai iya kai wa naira 729 a gidajen mai na jihar Lagos, idan gwamnatin Najeriya tabbas ta dakatar da biyan tallafin man.

A wasu sassan Najeriya ma, an fara ba da rahotannin samun karin kudin man fetur din a gidajen mai, ko da yake, har yanzu ba a ji wani bayani daga hukumomin Najeriya a kan wannan batu.

Shugaba Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur a cikin jawabinsa na kama mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023, lamarin da ya haddasa hauhawar farashi da matsin rayuwa.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp