fidelitybank

Farashin man fetur ya karu da kashi 55 – NBS

Date:

Hukumar kididdiga ta kasa ta ce, farashin man fetur ya ƙaru da kashi 55 a watan Janairu.

Wannan na kunshe ne cikin wani rahoto da hukumar ta fitar, inda ta ce a watan na Janairu, ‘yan Najeriya sun biya N257.12 a kan kowace lita.

Rahoton ya nuna cewa farashin a watan Janairun 2023 ya ƙaru da kashi 54.52 cikin 100 da kuma karuwar kashi 24.70 a kowane wata.

NBS ta kuma bayyana cewa jihar Imo ce ta fi kowace a sayar da litar man fetur, inda na ta ke a kan N332.14, sai Rivers a kan N327.14 da kuma Akwa-Ibom a kan N319.00.

Ta kuma lura da cewa Sokoto ce jihar da aka fi sayar da man fetur a kasan farashi, inda man fetur ɗin ke a kan N191.43 kan kowace lita, sai Filato a kan N192.14 da kuma Borno a kan N193.91.

‘Yan Najeriya da dama na ci gaba da biyan sama da N185 kan kowace lita da aka amince da shi a matsayin farashin man fetur sakamakon ƙarancin mai, kamar yadda rahoton hukumar kididdiga ta kasa ya nuna.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp