fidelitybank

Farashin kayan abinci ya yi tashin gauran zabi a Najeriya – NBS

Date:

Hukumar kididdiga ta kasa, ta ce, farashin kayan abinci ya tashi zuwa kashi 31 a cikin watanni 12 da suka gabata farawa daga watan Yulin 2022 zuwa Yulin 2023.

Cikin wani rahoto da NBS ɗin ta fitar kan ‘farashin kayan abinci’, ta ce jihohin Ebonyi da Abia ne aka fi samun hauhawar farashin.

A cewar rahoton, an fi samun tashin farashin ne a doya, wanda ya tashi da kashi 42, daga N389.75 a watan Yulin 2022 zuwa N539.41 a 2023.

NBS ta ce ba ya ga doya, sai kuma farashin shinkafa wanda ya tashi daga N467.80 zuwa N653.49 a cikin watanni 12.

Haka-zalika, farashin manja shi ma ya tashi da kashi 35 cikin 100, daga N890.67 zuwa N1208.62.

Sauran kayan abincin da farashinsu ya tashi sun haɗa da garin kwaki, wanda ya ƙaru da kashi 33 cikin 100, daga N323.17 zuwa N429.89, da kuma biredi wanda ya karu daga N486.27 zuwa N651.78.

Sauran sun haɗa da tumatir da Alkama da kuma nama.

Rahoton na NBS ya nuna cewa an fi samu tsadar kayan abinci a jihohin Kudu-maso-Gabas, musamman ma Abia da Ebonyi.

A ɗaya ɓangaren kuma, an samu mafi saukin farashin kayan abinci a jihohin Arewa ta Tsakiya da suka haɗa da Kogi, Neja, da kuma Benue.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp