fidelitybank

Farashin Fetur ya karye a Najeriya

Date:

Farashin man fetur ya karye a defo-defo na Najeriya a daidai lokacin da ake raɗe-raɗin ƙarin farashin man zuwa naira 700 a kan duk lita ɗaya cikin wannan wata na Yuli.

Ƙungiyar dillalan man fetur ta Najeriya, IPMAN ta tabbatar da karyewar farashin, ta ce ana sayar da shi a kan naira ɗari huɗu da ɗoriya, saɓanin sama da naira ɗari biyar a kan duk lita ɗaya.

Shugaban ƙungiyar reshen arewacin Najeriya, Bashir Ahmed Danmalam ya shaida wa BBC cewa farashin ya karye ne saboda ƙarancin masu saye, kuma za a samu rangwamen har a gidajen mai.

Danmalam ya ce tun kafin tafiya hutun sallah, farashin man fetur ɗin ya fara sauka.

“A yanzu haka, man fetur a defo-defo ɗin da ke Lagos da Warri da Calabar, an samu sauƙi domin ana (samun sa a kan) ƙasa da naira ɗari huɗu”.

Jami’in na IPMAN ya ce farashin man zai yi ƙasa a kwanaki masu zuwa a sassa daban-daban na Najeriya.

“A makon da muke ciki farashin zai yi ƙasa, sannan kuma ya kamata a san cewa yawan masu sayen man fetur ma ya ragu, ba kowa ne yake da kuɗin da zai iya sayen mai yanzu ba”.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp