Faransawa na gudanar da zagayen farko na zaɓen shugaban kasa, inda za su zaɓi tsakanin ‘yan takara goma 12.
Ƴan takara biyu da suka fi yawan ƙuri’a ne za su kai ga zagaye na biyu na zaɓen nan gaba a wannan watan.
Ƴan takarar da ke kan gaba a ƙuri’ar jin ra’ayi su ne shugaba Emmanuel Macron da shugabar masu ra’ayin riƙau Marine Le Pen, waɗanda sakamakon ya nuna za su iya lashe zaɓen.
Marine Le pen ya yi ta mayar da hankali a yaƙin neman zaɓenta kan bai wa Faransa fifiko a gidaje, da ayyukan yi da kuma tsaurara matakan tsaro.
Mista Macron da ya fi mayar da hankali kan yaƙin Ukraine, sai daga baya ne ya fara taɓo batutuwan da suka shafi cikin gida.
Idan har Macron ya lashe zaɓen zai kasance shugaba na farko, bayan Jacques Chirac da ya yi wa’adi na biyu a shekaru 20.
A 2017 aka zaɓi Marcon wa’adi na farko inda ya lashe zaɓen da gagarumin rinjaye.