Rukunin karshe na dakarun Faransa da ke aiki a Barkhane sun bar Mali a ranar Litinin, abin da ya kawo karshe kusan shekara 10 na hadin gwiwar ayyukan soji tsakanin kasashen biyu.
Rukunin karshe na sojojin su tsallaka iyakar Nijar, kuma sun je ne daga yankin Gao wanda ke hannun sojojin Mali.
Sanarwar barin sojojin ta zo ne jim kadan bayan masu fafutuka a Gao da kuma Bamako sun yi zanga-zanga indfa suka bukaci sojojin na Faransa da su bar kasar kafin ranar Laraba.
Masu fafutukar na zarginsu da goyawa masu tayar da kayar baya baya. In ji BBC.