fidelitybank

Faransa ta kori dan Osama Bin Laden wanda ya bijire masa daga kasar

Date:

Ministan harkokin cikin gida na Faransa ya ce ƙasar ta hana ɗan tsohon jagoran al-Qaeda, Osama Bin Laden komawa ƙasar ta Faransa.

Omar Bin Laden mai shekara 43 ya kwashe shekaru yana zaune a arewacin Faransa tare da matarsa, inda yake sana’ar zane-zane.

Ministan harkokin cikin gidan, Bruno Retailleau ya ce an hana Omar komawa ƙasar ne saboda wani rubutu a kafofin sadarwa da ke da alaƙa da tuna kashe mahaifinsa, wanda hukumomi a ƙasar suka ce yana ƙarfafa ‘gwiwar ta’addanci.’

Tun a shekarar 2023 Omar ya bar Faransa bayan an soke shaidar zamansa a sanadiyar rubutun.

A shekarar 2016 ce Omar Bin Laden ya koma zama a Faransa, bayan ya samu shaidar zama ɗan ƙasar ta hanyar auren wata ƴar Birtaniya mai suna Jane Felix-Browne, wadda ta koma Zaina Mohamed Al-Sabah.

Retailleau ya ce yanzu sun soke shaidar zamansa ɗan kasar, kuma ba sa buƙatar ya koma ƙasar ko da don wani dalilin ne.

Rahotanni na cewa yanzu ya koma Qatar ne da zama tare da matarsa. In ji BBC.

An haifi Omar ne a Saudiyya, kuma shi ne ɗan Osama na huɗu. Ya bar tafarkin mahaifinsa ne a shekarar 2000, inda ya ce shi bai amince da tsarin da ake kashe fararen hula ba.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp