fidelitybank

Faransa ta bukaci Isra’ila ta tsagaita wuta

Date:

Faransa ta yi kiran a tsagaita wuta cikin gaggawa kuma mai dorewa a yaƙin da Isra’ila ke yi da Hamas, tana cewa ta yi matuƙar damuwa da halin da ake ciki a Gaza.

Ministar harkokin wajen Faransa Catherine Colonna ce ta bayyana haka, inda ta ƙara da cewa ana kashe fararen hula da yawa da ba su ji ba ba su gani ba.

Firaiministan Isra’ila Elin Cohen ya ce tsagaita wutar zai zama kuskure, inda ya bayyana shi a matsayin wata kyauta ga Hamas.

Burtaniya da Jamus ma sun yi kira a tsagaita wutar ta dindindin, amma sun yi kiran a samar da gajeriya cikin gaggawa.

Mis Colonna ta isa Tel Aviv ranar Lahadi domin tattaunawa da takwaranta na Isra’ila Eli Cohen.

Cikin wata sanarwa da ta fitar gabanin ziyararta ta, Ministar harkokin wajen ta Faransa ta ce za ta yi kiran a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta har abada wadda za ta ƙunshi sakin mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma shigar da kayan agaji Gaza.

Cohen ya nanata manufar gwamnatinsu ta kin tsagaita wuta.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp