Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta goyon bayan kowanne yunƙuri na tilasta kifar da gwamnati a Iran.
Jean-Noel Barrot ne ya bayyana haka kafin taron ministocin harkokin wajen ƙungiyar Tarayyar Turai da aka gudanar a birnin Brussels.
Ya ce Iran kaɗai ce za ta iya yanke irin wannan hukunci, yana mai cewa bai kamata a yi tunanin cewa za a iya tilasta kifar da gwamnati da bama-bamai.
A baya dai, Shugaba Donald Trump ya ambato yiwuwar kifar da gwamnatin Iran.