fidelitybank

Fani Kayode ya kai karar tsohuwar matarsa kotu da yunkurin kisa

Date:

Tsohuwar matar tsohon ministan sufurin jiragen saman, Femi Fani-Kayode, ya maka tsohuwar matarsa Precious Chikwendu, a kotu da zarginta da kiransa da mai karamin azzakari kuma ta yi yunkurin hallaka shi da sabuwar budurwarsa.

Ya kara da bayyana cewa, sun yi amfani da yanar gizo wurin wallafa karairayi a kansa, inda ta ce, ya na duka tare da lalata da ‘yan aikinsa.

Jaridar Dailytrust ta rawaito cewa, ‘yan sandan sun gurfanar da Chikwendu a gaban mai shari’a, Inyang Ekwo kan zargin yunkurin kisan kai.

A karar mai lamba FHCABJ/CR/1/2022 wacce kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayyan ya shigar a kan Chikwendu da wasu mutum 3, an ce tsohuwar matar ta yi yunkurin soka wa Fani-Kayode wuka a ranar 24 ga watan Nuwamban 2018 a Asokoro.

Sauran wadanda aka gurfanar tare da Chikwendu sun hada da Emmanuel Anakan, Prisca Chikwendu da Osakwe Azubuike yayin da sauran ba a kamo su ba.

A zargi 13 da aka shigar, wadanda ake zargin a na tuhumarsu ne da laifuka da suka hada da hantara, yunkurin kisan Fani-Kayode da yunkurin kashe wata Lauretta wanda hakan yasa ta bar mu’amala da Fani-Kayode. A na zarginsu da yin amfani da shafin sada zumunta wajen aika sakonni cin zarafi da niyyar hantara da bata sunan tsohon mijinta.

Wadanda ake zargin sun musanta aikata laifukan da ake zarginsu da su wadanda abun hukuntawa ne a karkashin sashi na 392 na dokokin Penal Code.

Mai shari’a Ekwo ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 27 Afirilu, 28 Afirilu da 29 Afirilu.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maÆ™iya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp