Kimanin FalasÉ—inawa sama da dubu dari hudu ne suka tserewa gidajensu, sakamakon hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa Zirin Gaza.
Bakin hayaki ne ya turnuke sararin samaniyar birnin da aka shafe kwanaki biyu cir, cikin duhu sakamakon yanke musu wuta, da ruwa, da abinci, da man fetur da Isra’ilar ta yi.
Jami’an kiwon lafiya na FalasÉ—inawa sun ce akalla mutane arba’in da biyar ne suka mutu a lokacin da wani hari ta sama ya rutsa da wani rukunin gidaje a gundumar Jabaliya.
Ministan makamashi na Isra’ila ya ce ba za a bai wa Gaza wuta ba, har sai mayakan Hamas sun saki ‘yan Isra’ilar da suka kama.
Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar Amnesty International sun bayyana matakin na Isra’ila a matsayin laifin yaki.