Masu zanga-zanga Falasdinawa sun yi ta jifar jami’an tsaron Isra’ila da kujeru da wasu a Masallacin Kudus a daidai lokacin da Yahudawa ke wani tattaki da suke gudanarwa duk shekara mai cike da cece-kuce.
Bidiyo ya nuna ‘yan sanda sun yi amfani da sarka don rufe kofofin wurin ibadar yayin da masu zanga-zangar ke karuwa.
Idan an jima a yau ne dubban ‘yan Isra’ila za su daga tutoci a faretin da za su yi a yankunan Musulmitsohon birnin Kudus.
Taron na ɗaga tuta, Yahudawa na yin sa don murnar karbe Gabashin Jerusalam a yakin 1967, kuma wannan ya zo ne a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin Isra’ila da Falasdinawa.
Ana sa ran baza ƴan sanda kusan dubu uku a yankin. In ji BBC.
Isra’ila ta ɗauki birnin Kudus baki dayansa a matsayin babban birninta, yayin da Falasdinawa ke ikirarin gabashin birnin Kudus a matsayin babban birnin Falasdinu.