fidelitybank

Falasɗinawa 602 Isra’ila za ta saki a musayar Yahudawa shida

Date:

Hukumomin Isra’ila za su saki Falasɗinawa ɗari shida da biyu ne a musayar ‘yan ƙasarta shida da Hamas za ta saki a yau Asabar.

Tuni Hamas ta riga ta saki biyar daga cikin ‘yan Isra’ila shida da za ta saki a yau ɗin cikin waɗanda ta yi garkuwa da su.

Ɗan Isra’ila cikon na shida da Hamas ɗin za ta saki nan gaba a yau shi ne Hisham al-Sayed, wanda za a saki ba tare da wani taron jama’a ba, kamar yadda bayanai suka nuna.

Hamas ta kama shi ne tun shekara ta 2015 bayan da ya shiga yankin Gaza.

Rahotanni na nuna cewa tuni Red Cross ta danƙa wa rundunar sojin Isra’ila wasu daga cikin Yahudawan da aka saki yau, kuma sun shiga yankin Isra’ila.

Falasɗinawan da Isra’ila za ta saki 602 a yau, na daga matakin farko na yarjejeniyar dakatar da wuta, wadda ta tanadi cewa Isra’ila za ta saki Falasɗinawa fursunoni da waɗanda take tsare da su 1,900 a musaya da ‘yan Isra’ila 33 da Hamas ta yi garkuwa da su.

An saki sama da Falasɗinawa fursunoni 1,000 da Isra’ila take tsare da su, tun bayan da aka fara aiwatar da kashin farko na yarjejeniyar mai mataki uku, daga ranar 19 ga watan Janairun 2025.

Hukumomin Falasɗinu sun ce a makon da ya gabata Isra’ila ta saki fursunoni Falasɗinawa 369 – kuma 36 daga cikinsu na zaman ɗaurin rai da rai ne sannan ana tsare da 333 ba tare da wata tuhuma ba.

Yawancin Falasɗinawan da ta saki an kai su Gaza wasu an sake su ne a Gaɓar Yamma sannan galibin masu hukuncin ɗaurin rai da rai an fitar da su ne zuwa Masar.

Tun bayan harin ba-zata da Hamas ta kai wa Isra’ila a 2023, yawan Falasɗinawan da Isra’ila ke tsare da su ya ninka biyu zuwa wajen 10,000

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp