fidelitybank

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Date:

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi Falana ya caccaki manufofin tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu inda ya ce “manufofin masu tsauri” sun shafe masu matsakaicin samu tare da ƙara jefa miliyoyin mutanen ƙasar cikin talauci.

Falana ya ce duk da cewa a baya-bayan nan shugaban ƙasar ya fito ya bayyana cewa ya san irin halin ƙunci da ƴan Najeriya ke ciki, manufofinsa sun ƙara talauta al’umma.

Lauyan mai muƙamin SAN ya shaida hakan ne a hirar da ya yi a gidan Talabijin na Channels inda kuma ya ga baiken yadda gwamnati ke cefanar da kamfanoni ga ƴan kasuwa lamarin da a cewarsa ya ci karo da ƙoƙarin da ake na magance bambancin samu a tsakanin ƴan Najeriya.

Ya ƙara da cewa ya zama dole gwamnati ta sake nazari kan manufofinta tare da samar da tallafi ga ƴan Najeriya masu rauni musamman waɗanda suke yankunan karkara.

Lauyan ya bayyana cewa galibin ƴan Najeriya a yanzu ba sa iya cin abinci sau uku a rana.

“Dole gwamnati ta sake yin nazari kan waɗannan manufofin musamman waɗanda Bankin Duniya da Asusun ba da lamuni na duniya suka bijiro da su, domin ci gaban ƴan Najeriya. Ya kamata gwamnati ta sake nazarin waɗannan manufofin ba tare da ɓata lokaci ba.” in ji shi.

Tun bayan da ya hau karagar mulki a Mayun 2023, Tinubu ya sanar da wasu manufofin tattalin arziki ciki har da cire tallafin mai da barin kasuwa ta tsaida farashin naira.

Janye tallafin man dai ya janyo hauhawar farashin man abin da ya ƙara ta’azzara yanayin talauci da kuma ƙaruwar farashin sufuri har ma da hauhawar farashin kayan masarufi.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp