Fafaroma Francis ya yi kira da a ‘mutunta’ jami’an wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya da ke aiki a Lebanon.
Fafaroma ya bayyana haka ne bayan jikkata wasu jami’an MDD biyar a kudancin Lebanon.
“Ina kusa da dukkan mutanen da wannan abin ya shafa kama daga Falasɗinawa da Isra’ilawa da kume ƴan Lebanon, inda na buƙaci a mutunta jami’an wanzar da zaman lafiya,” in ji Fafaroma yayin da yake magana a fadarsa ta Vatican.
“Ina ƙara yin kira da a tsagaita wuta nan take tsakanin ɓangarori, sannan a bi matakin tattaunawa da kuma diflomasiyya domin samun zaman lafiya,” in ji shi.