fidelitybank

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Date:

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano Rabi’u Musa Kwankwaso martani kan ikirarinsa na cewa gwamnatin Bola Tinubu na nuna bambanci tsakanin yankunan ƙasar.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kan sadarwa, Sunday Dare ya fitar a yau Juma’a, ya ce, tun bayan hawan sa mulki, shugaba Tinubu ya gudanar da muhimman ayyuka da dama a Arewacin ƙasar da suka shafi harkoki daban-daban.

Ya bayar da misali da wasu ayyuka fiye da arba’in da ya ce gwamnatin Tinubu ta aiwatar, ko ke aiwatarwa a Arewacin ƙasar daga hawa kan mulki.

Daga cikin manyan ayyukan da ya lissafa akwai gina tituna da bangaren noma da bangaren lafiya da ayyukan ɓaagren makamashi da dai sauransu.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso dai ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da nuna wariya ga Arewacin Najeriya ta hanyar mayar da yawancin albarkatun ƙasar zuwa Kudancin ƙasar.

A wani taron masu ruwa da tsaki na jihar Kano da ya gudana a ranar Alhamis, Kwankwaso ya ce “Bayanai da muka samu na nuna cewa kamar rabin kasafin kuɗi na tafiya zuwa wani ɓangare guda a ƙasar nan,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso wanda ya yi wa jam’iyyar NNPP takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, ya zargi jam’iyyar APC da karkatar da albarkatun ƙasa tsakanin ɓangarori biyu na Najeriya.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp