fidelitybank

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Date:

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano Rabi’u Musa Kwankwaso martani kan ikirarinsa na cewa gwamnatin Bola Tinubu na nuna bambanci tsakanin yankunan ƙasar.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kan sadarwa, Sunday Dare ya fitar a yau Juma’a, ya ce, tun bayan hawan sa mulki, shugaba Tinubu ya gudanar da muhimman ayyuka da dama a Arewacin ƙasar da suka shafi harkoki daban-daban.

Ya bayar da misali da wasu ayyuka fiye da arba’in da ya ce gwamnatin Tinubu ta aiwatar, ko ke aiwatarwa a Arewacin ƙasar daga hawa kan mulki.

Daga cikin manyan ayyukan da ya lissafa akwai gina tituna da bangaren noma da bangaren lafiya da ayyukan ɓaagren makamashi da dai sauransu.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso dai ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da nuna wariya ga Arewacin Najeriya ta hanyar mayar da yawancin albarkatun ƙasar zuwa Kudancin ƙasar.

A wani taron masu ruwa da tsaki na jihar Kano da ya gudana a ranar Alhamis, Kwankwaso ya ce “Bayanai da muka samu na nuna cewa kamar rabin kasafin kuɗi na tafiya zuwa wani ɓangare guda a ƙasar nan,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso wanda ya yi wa jam’iyyar NNPP takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, ya zargi jam’iyyar APC da karkatar da albarkatun ƙasa tsakanin ɓangarori biyu na Najeriya.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp