fidelitybank

Fadar shugaban kasa ta magantu a kan sakin ɗaliban Kuriga 287

Date:

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan ceto daliban da aka sace daga yankin Kuriga da ke jihar Kaduna.

Mai bawa shugaban kasa Bola Tinubu shawara na musamman kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya godewa Allah da ya saki daliban, yayin da ya yabawa Gwamna Sani Uba.

Da yake aikawa a kan X, Onanuga ya rubuta: “Mun gode wa Allah da masu garkuwa da su suka sako yaran. Ina taya Gwamna Sani murna.”

Daliban makarantar Kuriga 287 da ‘yan bindiga suka sace kwanan nan a jihar Kaduna sun sami ‘yanci.

Gwamna Uba Sani ne ya bayyana haka a safiyar Lahadi.

Idan ba a manta ba, a ranar 7 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ke addabar jihar suka mamaye makarantar firamare ta LEA da ke garin Kuriga da ke karamar hukumar Chikun, inda suka yi awon gaba da dalibai 287 ciki har da wani shugaban makarantar Abubakar Isah zuwa inda ba a sani ba.

Maharan sun bukaci a biya su kudin fansa Naira biliyan daya a matsayin sharadin sakin yaran.

Babu tabbas ko jami’an tsaro ne suka ceto yaran ko kuma an biya su kudin fansa.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp