fidelitybank

Fadar shugaban kasa ta magantu a kan sakin ɗaliban Kuriga 287

Date:

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan ceto daliban da aka sace daga yankin Kuriga da ke jihar Kaduna.

Mai bawa shugaban kasa Bola Tinubu shawara na musamman kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya godewa Allah da ya saki daliban, yayin da ya yabawa Gwamna Sani Uba.

Da yake aikawa a kan X, Onanuga ya rubuta: “Mun gode wa Allah da masu garkuwa da su suka sako yaran. Ina taya Gwamna Sani murna.”

Daliban makarantar Kuriga 287 da ‘yan bindiga suka sace kwanan nan a jihar Kaduna sun sami ‘yanci.

Gwamna Uba Sani ne ya bayyana haka a safiyar Lahadi.

Idan ba a manta ba, a ranar 7 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ke addabar jihar suka mamaye makarantar firamare ta LEA da ke garin Kuriga da ke karamar hukumar Chikun, inda suka yi awon gaba da dalibai 287 ciki har da wani shugaban makarantar Abubakar Isah zuwa inda ba a sani ba.

Maharan sun bukaci a biya su kudin fansa Naira biliyan daya a matsayin sharadin sakin yaran.

Babu tabbas ko jami’an tsaro ne suka ceto yaran ko kuma an biya su kudin fansa.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp