fidelitybank

Fadar shugaban kasa ta caccaki wanda ke korafi a kan hukuncin Filato

Date:

Fadar shugaban kasa ta caccaki wadanda ke korafi kan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na korar Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato.

Mai bawa shugaban kasa Bola Tinubu shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya ce jam’iyyar PDP, ya kamata a dora wa laifin korar gwamnanta, Mutfwang ba shugaban kasa ko kuma bangaren shari’a ba.

Onanuga ya nuna cewa PDP ta yi amfani da kwamitin rikon kwarya ba bisa ka’ida ba wajen gudanar da zaben fidda gwani a jihar Filato, duk da umarnin kotu.

Kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin kotun zaben gwamnan da ta tabbatar da zaben Mutfwang a matsayin gwamnan jihar.

Kotun ta ayyana Dr Nentawe Yilwatda na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar yayin da ta umarci hukumar zabe ta kasa (INEC) da ta ba shi sabuwar satifiket din dawowar sa.

Da yake mayar da martani, Onanuga ya tuna yadda jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sha kaye a jihar Zamfara a shekarar 2019 kan zaben fidda gwani da aka yi ba bisa ka’ida ba.

Bugawa akan X tare da taken: “Kaddamar da Caleb Mutfwang za a iya kauce masa,” Onanuga ya rubuta: “Ga wadanda ke kuka da korafi game da hukuncin da Kotun daukaka kara ta yanke na soke zaben Gwamna Caleb Mutfwang, da alama sun manta da tarihi cikin sauri.

“A shekarar 2019, dukkan zababbun jami’an Zamfara da ‘yan jam’iyyar APC, tun daga gwamna zuwa jiha da kuma ‘yan majalisar dokoki ta kasa sun rasa mukamansu saboda APC ta kasa gudanar da zaben fidda gwani da doka ta tanada.

“Jam’iyyar PDP ta kasa koyi da tarihi, ta sake maimaita irin wannan haramcin, inda ta yi amfani da kwamitin riko ba bisa ka’ida ba wajen gudanar da zaben fidda gwani, duk da umarnin kotu.

“Ku dora wa PDP alhakin koma bayan zabe, ba APC, bangaren shari’a, INEC da kuma Shugaba Tinubu ba.

“Rashin bin dokar zabe da tsarin mulki shi ma shine tushen soke zaben gwamnan Kano, Abba Yusuf. Wadanda suke zargin bangaren shari’a da kuma jin haushin hukuncin ya kamata su fuskanci gaskiya. An kori Yusuf ne bisa doka. Na yi imani dukkanmu muna son kasarmu ta kasance mai bin doka da oda.”

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp