fidelitybank

Fadan makiyaya ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da cewa mutane biyu sun samu raunuka tare da yin awon gaba da shanu 16 a unguwar Takazza da ke karamar hukumar Guri ta jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Jigawa, Emmanuel Ekot Effiom, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ofishinsa a ranar Talata.

Ya ce, lamarin da ya faru a karshen makon da ya gabata a wani harin ramuwar gayya ne tsakanin al’umomin biyu a karamar hukumar Guri.

Kwamishinan ya bayyana cewa, an jikkata mutane biyu, an kuma lalata musu shanu 16, sannan an lalata wasu siloli a harin.

Ya ce an shirya sintiri na ‘yan sanda a yankin domin kwantar da hankulan lamarin inda suka yi nasarar cafke wasu mutane biyu tare da kwato shanu 11 da aka sace.

“’Yan sanda sun kama wasu mutane biyu da suka je sayar da sassan shanun a kasuwar Maigatari,” in ji shi.

Effiom ya ce ‘yan sanda suna bakin kokarinsu wajen ganin an kama sauran wadanda ake zargin tare da kwato sauran shanun da aka sace daga cikin al’umma.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa al’ummar Takazza sun dawo daidai da yadda aka baza jami’an tsaro a yankunan da abin ya shafa.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp