fidelitybank

Fadan makiyaya ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da cewa mutane biyu sun samu raunuka tare da yin awon gaba da shanu 16 a unguwar Takazza da ke karamar hukumar Guri ta jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Jigawa, Emmanuel Ekot Effiom, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ofishinsa a ranar Talata.

Ya ce, lamarin da ya faru a karshen makon da ya gabata a wani harin ramuwar gayya ne tsakanin al’umomin biyu a karamar hukumar Guri.

Kwamishinan ya bayyana cewa, an jikkata mutane biyu, an kuma lalata musu shanu 16, sannan an lalata wasu siloli a harin.

Ya ce an shirya sintiri na ‘yan sanda a yankin domin kwantar da hankulan lamarin inda suka yi nasarar cafke wasu mutane biyu tare da kwato shanu 11 da aka sace.

“’Yan sanda sun kama wasu mutane biyu da suka je sayar da sassan shanun a kasuwar Maigatari,” in ji shi.

Effiom ya ce ‘yan sanda suna bakin kokarinsu wajen ganin an kama sauran wadanda ake zargin tare da kwato sauran shanun da aka sace daga cikin al’umma.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa al’ummar Takazza sun dawo daidai da yadda aka baza jami’an tsaro a yankunan da abin ya shafa.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp