Jamiāai a kasar Sudan sun ce a kalla kusan mutane 50 ne suka rasa rayukansu a wani riki da ke da nasaba da na kabilanci a yankin Darfur da ke yammacin kasar.
Sun ce rikicin da ya faru a garin Kreinik ya barke ne sanadiyyar gardama kan wayar salula wanda ya rikide zuwa tashin hankali.
Fada tsakanin al’umomin Larabawa da sauran kabilu a yankin Darfur ya yi kamari a watannin baya-bayanan. A cewar BBC.
Majalisar Dinkin Duniya (MDD), ta ce kashi 30 cikin 100 na alu’mmar Sudan za su bukaci kayan agaji a badi wanda shi ne adadi mafi girma a cikin shekara 10 da suka gabata.