fidelitybank

Fada tsakanin El-Rufa’i da Uba Sani magajinsa waye mai gaskiya?

Date:

Wani rikici irin na siyasa ya hudo kai a jihar Kaduna da ke tsakiyar Najeriya, bayan da Gwamnan Jihar Uba Sani ya ce gwamnatinsa ba za ta iya biyan ma’aikata albashi ba saboda gagarumin bashin da ya gada daga Malam Nasir El-Rufa’i

Yayin wani taro da ya gudana a ranar Asabar a Kaduna, Uba Sani ya ce ya gaji bashin dala miliyan 587 kwatankwacin naira biliyan 85 ga kuma kudin kamfanonin ‘yan kwangila 115.

Ya ce an cire biliyan bakwai cikin 10 na kason da gwamnatin tarayya ta bai wa Kaduna a watan Maris biliyan bakwai ta tafi a biyan bashi.

Inda ya ara da cewa abin da ya yi wa jihar saura shi ne biliyan uku, ita kuma jihar tana biyan albashin biliyan 5.2 ne duk wata.

Ya ce tashin canjin kudi ya sanya jihar na biyan ninki uku na bashin da aka ci a baya.

“Duk da bashin da mukatarar da ya yi mana kanta, amma gwamnatina ba ta aro ko kobo ba a cikin watanni 9 di muka kwashe muna shugabanci

WaÉ—annan kalamai dai sun janyo martani daga ‘yan siyasar ciki da wajen jihar, kuma cikin waÉ—anda suka yi martanin har da É—an El-rufa’i Bashir.

Bashir El-Rufa’i ya rubuta a shafinsa na X cewa gwamna Uba Sani na neman fakewa da bashin ne ya rufe gazawa da kasawar gwamnatinsa.

Bashir ya yi ikirarin cewa gwamnan na neman sauka daga kai ayyukan da aka zaɓe shi a kai ya manta da aikin da ke gabansa,

“Wadannan sun tabbatar da cewa ba su cancanci wannan mulkin ba baki É—aya kuma hanya guda da za su boye hakan shi ne dauke hankalin mutane. Daga gwamnan da ya tare a Abuja ko da yaushe ya ke barci zuwa muÆ™arrabansa da aka naÉ—a muÆ™amai saboda dalilan siyasa na shiririta,” kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X.

Wannan dambarwa ta sanya mutane tunanin ko an sa zare ne tsakanin gwamna mai ci da wanda ya gaba? In ji BBC.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp