fidelitybank

Facebook zai fara biyan ‘yan kasar Ghana bayan sun wallafa hoton bidiyo a shafukan su

Date:

Masu ƙirƙirar bidiyo don wallafawa a dandalin sada zumunta na Meta a Ghana na ci gaba da bayyana murnarsu, kan matakin kamfanin na amincewa a fara biyan ƴan ƙasar masu ɗora bidiyo a shafinsu na Facebook.

Daman tun a baya kamfanin na Meta mai Facebook da Instagram da WhatsApp ya sanar da cewa daga ranar 1 ga watan Yuli na 2024 zai fara biyan wadanda suka cancanta, da ke sanya hotunan bidiyo a shafukansu na Facebook.

Ana sa ran wannan matakin zai haifar da bunƙasar tattalin arziki, tare da samar da dubban ayyuka ga mutane musamman matasa yayin da ake fuskantar matsanancin rashin aikin yi a kasat ta yammacin Afirka.

An dade ana fatan ganin ranar da daya daga cikin manyan kamfunan sada zumunta a duniya na Facebook zai fara biyan `yan kasar ta Ghana masu kirkiro bidiyo suna dorawa a kan shafin.

Dubban matasa ne a Ghana suka rungumi sana`ar kirkiro bidiyo suna wallafawa a kan intanet don rufa wa kai asiri yayin da matsalar rashin aiki ta yi kamari.

Duk da yake masana na son barka da wannan cigaba amma suna kiran gwamnati da ta kara jajircewa a wajen sa ido a kan irin abubuwan da masu kirkio bidiyo za su rinka dorawa a kan shafukansu.

Musamman yayin da ake shirin gudanar da babban zaben kasar ta Ghana a watan Disamba mai zuwa, ganin cewa wasu ka iya amfani da wannan dama wurin yada farfaganda ko labaran kanzon-kurege da cin zarafi, ko kyama, wanda haka zai iya janyo tarzoma.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp