fidelitybank

Facebook zai fara biyan ‘yan kasar Ghana bayan sun wallafa hoton bidiyo a shafukan su

Date:

Masu ƙirƙirar bidiyo don wallafawa a dandalin sada zumunta na Meta a Ghana na ci gaba da bayyana murnarsu, kan matakin kamfanin na amincewa a fara biyan ƴan ƙasar masu ɗora bidiyo a shafinsu na Facebook.

Daman tun a baya kamfanin na Meta mai Facebook da Instagram da WhatsApp ya sanar da cewa daga ranar 1 ga watan Yuli na 2024 zai fara biyan wadanda suka cancanta, da ke sanya hotunan bidiyo a shafukansu na Facebook.

Ana sa ran wannan matakin zai haifar da bunƙasar tattalin arziki, tare da samar da dubban ayyuka ga mutane musamman matasa yayin da ake fuskantar matsanancin rashin aikin yi a kasat ta yammacin Afirka.

An dade ana fatan ganin ranar da daya daga cikin manyan kamfunan sada zumunta a duniya na Facebook zai fara biyan `yan kasar ta Ghana masu kirkiro bidiyo suna dorawa a kan shafin.

Dubban matasa ne a Ghana suka rungumi sana`ar kirkiro bidiyo suna wallafawa a kan intanet don rufa wa kai asiri yayin da matsalar rashin aiki ta yi kamari.

Duk da yake masana na son barka da wannan cigaba amma suna kiran gwamnati da ta kara jajircewa a wajen sa ido a kan irin abubuwan da masu kirkio bidiyo za su rinka dorawa a kan shafukansu.

Musamman yayin da ake shirin gudanar da babban zaben kasar ta Ghana a watan Disamba mai zuwa, ganin cewa wasu ka iya amfani da wannan dama wurin yada farfaganda ko labaran kanzon-kurege da cin zarafi, ko kyama, wanda haka zai iya janyo tarzoma.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp