Hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa FAAN, ta sanar da rufe titin jiragen sama na kasa da kasa 18R da 36L a filin jirgin Murtala Muhammed da ke Legas domin kula da su wajen yin gyara.
FAAN ta sanar da hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.
FAAN ta ce za a rufe hanyoyin saukar jiragen har na tsawon makonni takwas domin kula da su.
Karanta Wannan:Â Jirgin saman sojin Najeriya ne ya kai hari Shiroro – Gwamnatin Neja
Sanarwar ta kara da cewa “Wannan shine don sanar da jama’a cewa an rufe titin jirgin sama mai lamba 18R/36L na filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas tsawon makonni takwas domin gudanar da aikin.
A cewar hukumar, Taxiway B-18L za a yi amfani da shi a maimakon duk ayyukan jirgin har sai an kammala gyarawa.