fidelitybank

Faɗan ƙabilanci ya yi sanadiyar mutuwar mutane a Taraba

Date:

Ana fargabar cewa mutane da dama ne suka rasu a wani faɗa tsakanin Kuteb da Fulani makiyaya a cikin ƙaaramar hukumar Ussa ta jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa “Duk da yake, ba a san musabbabin rikicin ba, amma wani ganau ya ce ƴan ƙabilar Kuteb ne suka zargi Fulani da kai hari kan mutanensu, abin da ya haddasa kisan kai da kuma yin garkuwa da wasu”.

Ganau ɗin ya ce hakan ta sa ‘yan ƙabilar Kuteb suka kai wa Fulani hari a Kwe Sati, jiya Alhamis, abin da ya sa faɗan ya bazu zuwa garin Fikye in ji shaidan.

Ana kyautata zaton cewa mutane da yawa sun rasu.

Jagoran ƙungiyar al’ummar Kuteb, Emmanuel Ukwen, ya faɗa wa Daily Trust cewa an samu asarar rayuka daga dukkan ɓangarorin kabilun biyu.

Ya ce mutane sun tsere wa yankin yayin da ake ci gaba da faɗa, inda kuma aka ƙona gidaje da dama.

Rahotanni sun ce an kai hari gidan Sarkin Lisam Kwe, Ando Madugu, inda wasu fusatattun matasa suka ƙona fadarsa bayan sun zarge shi da mara wa Fulani baya.

A cikin makon nan ne, shugaban ƙaramar hukumar ta Ussa, Abershi Musa, ya yi murabus, bayan ya zargi gwamnatin jihar da kasa ɗaukar mataki a kan kashe-kashen mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, da ya zargi Fulani da yi.

Lokacin da aka tuntuɓi shugaban ƙungiyar Miyetti Allah na ƙaramar hukumar, Alhaji Bello, ya ce ba zai yi magana kan lamarin ba a halin yanzu.

Shi ma, mai magana da yawun ƴan sandan jihar, SP Usman Abdullahi, ba a same shi ba lokacin da aka kira wayarsa don ji daga gare shi game da wannan al’amari.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp