Kungiyar kwallon kafa ta Everton ta firimiyar Ingila ta Sean Dyche a matsayin sabon kocinta.
Masu kungiyar sun nada Dyche na tsawon shekara biyu da rabi, kwantiragin da za ta kawo karshe a watan Yunin 2025.
Kungiyar wadda masoyanta ke kira da sunan “Toffees” ta sallami Frank Lampard ne a makon jiya bayan da ta sami kanta a matsayi na 19 a teburin firimiya a karkashin kulawarsa.
Dyche mai shekara 51, kwararren koci ne wanda tun watan Afrilu ya zama ba shi da kulob din da yake horarwa tun da kungiyar Burnley ta sallame shi bayan ya shafe shekara 10 yana aiki tare da su.
Sean Dyche zai zama koci na bakwai a karskashin mai kungiyar Farhad Moshiri – wanda ya sayi kungiyar tun 2016.