Tottenham Hotspur na tunanin daukaka kara kan hukuncin da UEFA ta yanke na baiwa Rennes nasara da ci 3-0 bayan da a ka dage wasansu na gasar cin kofin Europa kuma sun fice daga gasar.
An yanke hukuncin cewa Tottenham ta rasa wasan kamar yadda su ka dakatar da shi, saboda karuwar Korona.
Koci Antonio Conte ya ce, kungiyar na magana da lauyoyin ta game da hukuncin.
“Ba tabbatacce ba ne, amma akwai wani mataki na tabbatarwa ko a’a wannan yanke shawara mai ban mamaki,” inji shi.
“Muna da kwarin gwiwa sosai a mataki na gaba kuma na sake maimaita cewa mun cancanci buga wasan. Ba zan iya yarda da hakan ba, mun ji takaicin UEFA da wannan hukuncin”.
“Hakika rashin adalci ne, mun cancanci buga wasan, domin mun ji takaicin matakin da hukumar ra ta dauka”. A cewar Conte.