Firaministan Hungary ya zargi Majalisar Tarayyar Turai da son rai kan batun dakatar da sayen mai daga Rasha daga nan zuwa karshen shekara.
Victor Orban ya ce, an wuce gona da iri wurin daukar wannan mataki, kuma a kan haka kasarsa za ta bijire.
Mista Orban ya ce ba zai bari Hungary ta shiga mummunan matsin tattalin arziki ba don dai EU ta samu nasarar ƙuntata wa Rasha.
Ya ce: “Mun fahimci cewa wannan Æ™udirin bai duba bambanci tsakanin kasashen EU ba, kuma abu ne da ba zai yiwu ba, don matsawar aka hana mu sayen man Rasha a wannan gabar tamkar an harba wa tattalin arzikinmu makamin nukiliya ne.”
Amma Ministan KuÉ—i na Ukraine Sergii Marchenko ya ce yanzu ne EU ya kamata ta É—auki matakin yanke sayen mai daga Rasha kwatakwata. A cewar BBC.