A jiya ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele, ya isa gidansa da ke Abuja, bayan da wata babbar kotun Abuja ta bayar da belinsa.
Ya shafe kwanaki 151 a hannun jami’an tsaro.
Babbar kotun tarayyar da ke zamanta a Maitama ta bayar da umarnin a sake shi daga gidan yari, duk da rashin amincewar da babban lauyan gwamnatin tarayya, AGF, da hukumar yaki da cin-hanci da rashawa EFCC suka yi.
Kotun, a hukuncin da mai shari’a Olukayode Adeniyi ya yanke, ta bayar da umarnin a saki tsohon gwamnan babban bankin ga lauyoyinsa, duk da cewa ta umarce shi da ya miƙa dukkan takardun tafiye-tafiyen sa na kasashen waje