fidelitybank

El-Rufa’i ya yi watsi da kalaman Buhari akan tsofaffin kudi

Date:

Gwamnan Jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai, ya umarci al’ummar jihar da su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗi na naira 500 da 1000, bayan da shugaba Buhari ya jaddada matsayin Babban Bankin ƙasar na soke amfani da kuɗin.

A wani jawabi da gwamnan ya yi ga al’ummar jihar a jiya Alhamis, jawabin da ke zama kamar na ƙalubalantar shugaban ƙasar, ya bayyana shirin canja kuɗin a matsayin wani makami da jiga-jigan jam’iyya mai mulki da mkusantan Shugaba Buhari suka ɓullo da shi domin dakatar da ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Bola Tinubu nasara a zaben 25 ga watan nan na Fabrairu.

Gwamnan ya bayyana shirin a matsayin na rashin imani, wanda ya haddasa talakawan ƙasar tsananin wahala, waɗanda ya ce su ne shirin ya tagayyara.

Ya ce shugabancin Babban bankin ƙasar, CBN, ya yaudari Shugaba Buhari da cewa an ɓullo da shirin ne da nufin daƙile ‘yan siyasa da suka tara maƙudan kuɗade domin sayen ƙuri’a lokacin zaɓe.

Gwamnan y bai wa al’ummar jihar tabbacin su ci gaba da amfani da takardun kuɗin kamar yadda ya ce Kotun Kolin kasar ta bayar da umarni.

Ya ce babu wani wa’adi da zai sa kuɗin su daina aiki, yana mai umartar jama’a su ci gaba da amfani da kuɗin, inda ya ce bayan zaɓe shi da sauran ‘yan majalisa zaɓaɓɓu da hukumomin gargajiya za su tattara kuɗin daga hannun jama’a su mika su ga Babban Bankin domin a sauya su.

Ya ce doka ta tabbatar da cewa ko da nan da shekara 100 ne, duk lokacin da aka kai tohon kuɗi ɓ dole ya sauya ya bayar da sabo.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp