fidelitybank

El-Rufa’i ya yi watsi da kalaman Buhari akan tsofaffin kudi

Date:

Gwamnan Jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai, ya umarci al’ummar jihar da su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗi na naira 500 da 1000, bayan da shugaba Buhari ya jaddada matsayin Babban Bankin ƙasar na soke amfani da kuɗin.

A wani jawabi da gwamnan ya yi ga al’ummar jihar a jiya Alhamis, jawabin da ke zama kamar na ƙalubalantar shugaban ƙasar, ya bayyana shirin canja kuɗin a matsayin wani makami da jiga-jigan jam’iyya mai mulki da mkusantan Shugaba Buhari suka ɓullo da shi domin dakatar da ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Bola Tinubu nasara a zaben 25 ga watan nan na Fabrairu.

Gwamnan ya bayyana shirin a matsayin na rashin imani, wanda ya haddasa talakawan ƙasar tsananin wahala, waɗanda ya ce su ne shirin ya tagayyara.

Ya ce shugabancin Babban bankin ƙasar, CBN, ya yaudari Shugaba Buhari da cewa an ɓullo da shirin ne da nufin daƙile ‘yan siyasa da suka tara maƙudan kuɗade domin sayen ƙuri’a lokacin zaɓe.

Gwamnan y bai wa al’ummar jihar tabbacin su ci gaba da amfani da takardun kuɗin kamar yadda ya ce Kotun Kolin kasar ta bayar da umarni.

Ya ce babu wani wa’adi da zai sa kuɗin su daina aiki, yana mai umartar jama’a su ci gaba da amfani da kuɗin, inda ya ce bayan zaɓe shi da sauran ‘yan majalisa zaɓaɓɓu da hukumomin gargajiya za su tattara kuɗin daga hannun jama’a su mika su ga Babban Bankin domin a sauya su.

Ya ce doka ta tabbatar da cewa ko da nan da shekara 100 ne, duk lokacin da aka kai tohon kuɗi ɓ dole ya sauya ya bayar da sabo.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp