fidelitybank

El-Rufa’i ya yashe Kaduna ya bar talakawa cikin kunci – Shehu Sani

Date:

Tsohon dan majalisa, Sanata Shehu Sani, ya yi zargin cewa gwamnatin da ta shude a karkashin Nasir El-Rufai ta bar wa ‘ya’yansu gidaje da kantuna, tare da barin tudun mun tsira ga ‘ya’yan talakawa a jihar Kaduna.

Bayanin hakan na zuwa ne a daidai lokacin da wani kwamitin wucin gadi na majalisar dokokin jihar Kaduna ya gabatar da bukatar a binciki yadda yake tafiyar da mulkin jihar daga watan Mayun 2015 zuwa watan Mayun 2023.

A cewar rahoton, yawancin rancen da aka samu a karkashin gwamnatin El-Rufai, ba a yi amfani da su ba ne a dalilin da ya sa aka samu su, yayin da a wasu lokutan kuma ba a bi ka’idojin da ya kamata wajen samun lamunin.

Sai dai tsohon gwamnan ya mayar da martani inda ya nanata cewa ya jagoranci gwamnati mai gaskiya da iya aiki a gwamnatinsa na shekaru takwas.

El-Rufai ya ce rahoton aiki ne na siyasa, inda ya dage cewa ya yi aiki da gaskiya.

Duk da haka, Sani, a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Alhamis, ya ce bai san ma’anar “bauta da gaskiya ba”.

Ya ba da shawarar cewa mataki na gaba shi ne tabbatar da kwato kudaden da aka sace daga leda da ungulu.

“‘Majalisar Kaduna ta yi aiki mai kyau. Ina taya su murna, mataki na gaba shi ne tabbatar da kwato kudaden da aka sace daga wadannan leda da ungulu. ‘Yan damfara da masu ba da shawara na barayi da ‘yan kwangila da ke zaune a gidan Sir Kashim Ibrahim sun wawashe jihar Kaduna. Ga duk wanda ya damu ya bi wannan rahoton da aka buga, ban san ma’anar “bautawa da gaskiya ba”. Kaduna ta kasance an sha fama da ‘yan fashi iri biyu; na dazuzzukan mu da na gidan gwamnati.Sun bar wa ’ya’yansu gidaje da kantuna sun bar wa ’ya’yan talakawa bashin tudun mun tsira,” in ji Sabi.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp