fidelitybank

El-Rufa’i ya jinjina wa Sojoji kan kisan Isah Ɗan Wasa

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya jinjina wa dakarun sojin ƙasa da ke aiki a jiharsa, kan kisan wani fitaccen ɗan fashin daji mai suna Isiya Danwasa.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar, ya ce dakarun sojin sun kashe ɗan fashin dajin a yankin sabon birni na ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar.

Isiya Danwasa dai fitaccen ɗan fashin daji ne da ya addabi jihar da satar mutane domin neman kuɗin fansa, da fashi da kuma satar shanu.

Daga ƙarshe gwamnan ya yi kira ga mazauna jihar da su ci gaba da bai wa jami’an tsaron sahihan bayanai da za su fallasa ɓata-garin.

A nasu ɓangare kuma jami’an sojin Najeriya da ke aiki a ƙarƙashin rundunar Operation FOREST SANITY da ake Kaduna tare da haɗin gwiwwar dakarun shalkwatar rundunar tsaro ta ƙasar sun ce sun kama wani yaron jagoran ‘yan fashin daji a garin Mando a yankin ƙaramar hukumar Igabi.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin na Tuwita ta ce jami’anta sun kama yaron ‘yan fashin ne a lokacin da ubangidan nasa ya aike shi domin sayen harsasai a cikin gari.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp