fidelitybank

El-Rufa’i ya jinjina wa Sojoji kan kisan Isah Ɗan Wasa

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya jinjina wa dakarun sojin ƙasa da ke aiki a jiharsa, kan kisan wani fitaccen ɗan fashin daji mai suna Isiya Danwasa.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar, ya ce dakarun sojin sun kashe ɗan fashin dajin a yankin sabon birni na ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar.

Isiya Danwasa dai fitaccen ɗan fashin daji ne da ya addabi jihar da satar mutane domin neman kuɗin fansa, da fashi da kuma satar shanu.

Daga ƙarshe gwamnan ya yi kira ga mazauna jihar da su ci gaba da bai wa jami’an tsaron sahihan bayanai da za su fallasa ɓata-garin.

A nasu ɓangare kuma jami’an sojin Najeriya da ke aiki a ƙarƙashin rundunar Operation FOREST SANITY da ake Kaduna tare da haɗin gwiwwar dakarun shalkwatar rundunar tsaro ta ƙasar sun ce sun kama wani yaron jagoran ‘yan fashin daji a garin Mando a yankin ƙaramar hukumar Igabi.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin na Tuwita ta ce jami’anta sun kama yaron ‘yan fashin ne a lokacin da ubangidan nasa ya aike shi domin sayen harsasai a cikin gari.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp